Showing posts with label Labarai. Show all posts
Showing posts with label Labarai. Show all posts

Wednesday, November 21, 2018

Labaran duniya ::: Ku kalli kifin da ya hadiye kilo shida na robobi

Jami'ai sun ce an gano wajen kilo shida na robobi a cikin wata matacciyar giwar teku wadda ruwa ya turo ta gabar teku a wani gandun daji da ke Indonesia.
An gano kofunan roba 115 da robobin ruwa hudu da ledoji 25 da kuma takalman roba biyu a cikin giwar tekun.
An gano gawar giwar tekun mai tsawon mita 9.5 a cikin tekun da ke kusa da tsibirin Kapota a gundun dajin Wakatobi a ranar Litinin.
Ana binciken halittun da matukiyar jirgi ta gani a sama
Biri ya kashe wani jariri a Indiya
Kifi ya kashe wani mutum bayan ya cece shi
Gano giwar tekun ya haifar da damuwa tsakanin masu fafutukar kare muhalli.
Kamfanin dillancin labarai na AP ya ce Dwi Suprapti, wata jami'a da ke kare hakkokin dabbobin ruwa a WWF a Indonesia, ta ce: "Ko da yake ba mu iya gano dalilin mutuwar giwar tekun ba, amma abubuwan da muka gani da idanuwanmu ba su da kyawun gani."
Ta kuma kara da cewa ba zai yiwu a ce robobin da giwar ta hadiye ne dalilin da ya haifar da mutuwar giwar ba saboda yanayin rubewar da ta yi.
A cikin wani sakon da asusun tallafin gandun daji WWF ya wallafa a shafinsa na Twitter ya yi bayani dalla-dalla kan abubuwan da aka gano a cikin dabbar:
"Roba mai karfi (guda 19 mai nauyin giram 140) da kwalaben roba (guda 4 masu nauyin giram 150) da jakankunan roba (guda 25 masu nauyin giram 260) da takalman roba (guda 2 masu nauyin giram 270) da zararruka masu nauyin kilogiram 3.26 da kuma kofunan roba (guda 115 masu nauyin giram 750). "

Labarai duniya :: An sanya dokar hana fita a wasu yankuna a Bauchi

Gwamnatin jihar Bauchi da ke arewa maso gabashin Najeriya ta ce ta sanya dokar hana fita da daddare sakamakon rikicin da ya barke a birnin Bauchi.
Mai magana yawun gwamna Abubakar Mohammed, Malam Ali M. Ali, ya shaida wa BBC cewa "an hana fita tsakanin karfe bakwai na dare zuwa shida na safiya" sanadiyar fadan da ya kai ga mutuwar mutum uku.
Lamarin ya faru ne lokacin da aka samu rashin jituwa tsakanin matasan da suke bikin tunawa da ranar haihuwa kan wata budurwa, amma fadan ya rikide zuwa na kabilanci da siyasa.
Ba za a yi zabe ba sai an dakatar da gwamnan Bauchi - 'Yan takara
Giwaye sun kashe mutane a Bauchi
Abubuwa biyar da ba su da dadi a mulki - Gwamnan Bauchi
Dokar hana fitar ta shafi unguwannin Kagadama da Lushi da Tsakani da Kusu da kuma Anguwan Ngas da ke yankin Yalwa a cikin birnin na Bauchi.
Wanne ne karon farko da aka samu irin wannan yamutsi da ya yi dalilin mutuwar mutane tun da gwamnan jihar ya hau kan mulki shekara uku da rabi da suka wuce, in ji mai magana da yawunsa.
Ya yi kira da mazauna jihar su ci gaba da zama lafiya da juna.
Tuni dai gwaman jihar ya kai ziyara yankunan da lamarin ya shafa.
Gwamna M A ya kuma ce gwamnati za ta yi iyakar kokarinta don ganin rikicin bai yadu a wasu wuraren ba.
Jihar Bauchi dai na daga cikin jihohin da ba a faye samun tashe-tahsen hankula kowane iri ba a Najeriya.

Monday, July 23, 2018

Labaran duniya :: Ambaliya ta kashe mutum 13 ta raba 17,000 da muhallansu a Nijar

A kalla mutum 13 ne suka rasa rayukansu wasu 13 kuma suka jikkata sakamakon ambaliyar ruwan sama kamar da bakin kwarya da aka yi ta shatatawa a 'yan kwanakin nan a jihohin Maradi, Agadez da kuma Diffa a Jamhuriyar Nijar.
Wata sanarwa da hukumar agajin gaggawa ta Majalisar Dinkin Duniya OCHA ta fitar ta ce, wasu mutanen da yawansu ya kai 17,000 sun rasa muhallansu.
Sanarwar ta ce a ranar 18 ga wannan wata na Yuli ruwan sama ya hadassa asarar rayuka da ta dukiyoyi a wasu yankunan kasar.
An kiyasta cewa eka 400 ta kasar noma ta lalace sannan dabbobi 24,000 sun mutu sakamakon ambaliyar.
Ambaliyar Katsina: Ruwa ya tafi da jaririya 'yar wata uku
An hana 'yan agajin kungiyar Izala sa inifom a Nijar
Ambaliyar ruwa ta kashe mutum 40 a Katsina
A tsakiyar watan da ya gabata ne dai hukumar ta Majalisar Dinkin Duniya ta yi hasashen cewa akwai yiwuwar Jamhuriyar Nijar ta fuskanci matsalar ambaliyar da ka iya shafar a kalla mutum 170,000 a jihohin Dosso da Niamey, inda kogin Nijar ya ratsa.
Duk da cewa daminar wata uku kadai ke yi kuma ba a samun ruwa mai yawa, kasar na fuskantar matsalar ambaliya a 'yan shekarun baya-bayan nan.
Ko a shekarar da ta gabata ma mutum sama da 50 suka gamu da ajalinsu biyo bayan ambaliyar ruwa, yayin da wasu 206,000 suka rasa matsugunansu,sannan heka 9800 ta kasar noma ta salwanta.
Gwamnatin jamhuriyar Nijar ta ce ta saka makudan kudade da kusan CFA biliyan uku tare da taimakon Bankin Duniya don gina shingayen da za su hana kwararar ruwan zuwa gidajen da ke bakin kogin Nijar a Yamai, a matsayin riga-kafi.
Gwamnatin dai ta ce tuni ta kamala wannan aiki.

Thursday, July 27, 2017

Duniyar mu a yau

KYAUTAR ALLAH TAFI TA KOWA
Akwai wani sarki a kasar Habasha kullum idan ya fito zaure sai ya sami wasu mabarata wato masu bara guda biyu a kofar zaure. Kullum idan sarki ya fito sai yaji mabaraci na farko yana cewa "KYAUTAR SARKI TAFI TA KOWA" sai mabaraci na biyun kuma yace "KYAUTAR ALLAH TAFI TA KOWA", idan sarki kuma yaji zancen na farkon sai yaji dadi, amma idan yaji zancen mabaraci na biyun sai ransa ya baci.
.
Ana nan a haka rannan sarki ya fito zaure kamar yadda ya saba, fitarsa keda wuya sai yaji mabaratan sunzo yin bararsu kamar yadda suka saba, mabaraci na farko yace "KYAUTAR SARKI TAFI TA KOWA", na biyu kuma ya amsa "KYAUTAR ALLAH TAFI TA KOWA", sarki yana jin haka sai ya kira mabaraci na farko wato wannan mai cewa kyautar Sarki tafi ta kowa, sarki ya shiga ya dauko wani abu kamar gurasa ya baiwa mabaracin, bayan mabaracin ya fito ya sami dan uwansa a tsaye a waje sai ya nunawa dan uwan nasa gurasar da sarki ya bashi, sa'annan ya fadawa dan uwan nasa cewar shi ya zata ma kudi sarki zai bashi saboda yafi son kudi, daga nan ya sayarwa mabaraci na biyun gurasar akan fam biyar.
Bayan mabaraci na biyun ya koma gida ya dauki gurasar domin yaci, bude cikin gurasar keda wuya sai yaga ZINARI a cike a cikin gurasar, cikin farin ciki ya daga hannunsa sama ya godewa Allah yana mai cewa "KYAUTAR ALLAH TAFI TA KOWA".
Washe gari sarki ya fito zaure kamar yadda ya saba sai yaji mabaraci na farko yana cewa "KYAUTAR SARKI TAFI TA KOWA" sarki ya jira yaji muryar mabaraci na biyu kamar yadda ya saba amma baiji ba, sai ya fito ya leka ya tambayi mabaraci na farkon ina dan uwansa ? Sai yacewa sarki "NI BAN GASHI BA YAU, KUMA BAN SAN GIDANSA BA, DAMA A KOFAR GIDAN NAN MUKA SABA HADUWA SAI MU SHIGO TARE.
Sarki yace "Amma ga alama dai baka bude cikin gurasar dana baka jiya ba har yanzu ko ? Mabaracin ya risina yace "RANKA YA DADE BANCI BA, HASALI MA NAFI BUKATAR KUDI NE SHI YASA NA SAYARWA DAN UWANA MABARACIN NAN GURASAR"
Sarki ya dafe kai yace "Kash ! Baka da rabo, ai na sanya maka Zinari a ciki saboda in gaskata zancenka cewar KYAUTAR SARKI TAFI TA KOWA", koda mabaracin yaji haka sai ya fadi ya suma, sarki kuwa cikin sanyin jiki yace "HAKIKA KYAUTAR ALLAH TAFI TA KOWA"
.
ALLAH KA BAMU KYAUTAR NI'MARKA A DUNIYA SA'ANNAN KA SANYAMU CIKIN DAUSAYIN RAHMARKA A KIYAMA...