Thursday, January 17, 2019


Thursday, January 10, 2019

Wednesday, November 21, 2018

My Choice


Rulling Party

https://awwalkano.blogspot.com/2018/11/labaran-siyasa-yan-sandan-najeriya-sun.html?m=1

Labaran siyasa :: 'Yan sandan Najeriya sun gargadi APC da PDP

Rundunar 'yan sandan Najeriya ta gargadi 'yan siyasa na jam'iyyu daban-daban ciki har da APC da PDP su guji tayar da husuma lokacin yakin neman zaben 2019.
Sanarwar da mai magana da yawun rundunar 'yan sandan kasar Jimoh Moshood ya aike wa manema labarai ta babban sufeton 'yan sandan kasar Ibrahim Idris, ya ce zai dauki dukkan matakan da suka dace domin ganin zaben ya gudana ba tare da tashin hankali ba.
"Muna bai wa dukkan jam'iyyu umarni da su yi biyaya ga dokokin zabe. Su tabbatar sun gargadi masu yin takara a karkashinsu da masu goyon bayansu da kada su tayar da tarzoma" idan ba haka ba za su dandana kudarsu.
PDP ta zargi APC da 'murkushe abokan hamayyar siyasa'
Zaben Najeriya: An soma fafatawa tsakanin Atiku da Buhari
Nigeria: An sassari mutane a hawan Daushen Kano
Mr Moshood ya kara da cewa babban baturen 'yan sandan kasar ya umarci kwamishinonin 'yan sandan kasar 36 da na Abuja da kuma mataimakansa na shiyya 12 su tabbatar da tsaro a wuraren yakin neman zabe.
Kazalika, rundunar ta umarci 'yan sandan su guji shiga harkokin siyasa domin su kare martabarsu.
"Rundunar 'yan sanda ba za ta lamunci yin kalaman batanci da na tayar da husuma wadanda ka iya haddasa tashin hankali daga kowanne mutum lokacin yakin neman zabe da bayan sa ba,' in ji Mr Moshood.
A cewarsa, dole sarakuna da iyaye su ja kunnuwan 'ya'yansu game da shiga bangar siyasa, yana mai cewa rundunarsu za ta hukunta duk mutumin da aka samu da hannu wurin tayar da hankali.
Ranar Lahadin da ta gabata ne dai aka soma yakin neman zaben shugaban kasa a Najeriya.
'Yan takara sama da 30 ne za su fafata a zaben shugaban kasar, ko da yake masu sharhi na ganin fafatawar za ta fi yin zafi tsakanin Alhaji Atiku Abubakar na jam'iyyar PDP da Shugaba Muhammadu Buhari na jam'iyyar APC, wanda ke son yin wa'adi na biyu na mulki.
Karin labaran da za ku so ku karanta

Labaran duniya ::: Ku kalli kifin da ya hadiye kilo shida na robobi

Jami'ai sun ce an gano wajen kilo shida na robobi a cikin wata matacciyar giwar teku wadda ruwa ya turo ta gabar teku a wani gandun daji da ke Indonesia.
An gano kofunan roba 115 da robobin ruwa hudu da ledoji 25 da kuma takalman roba biyu a cikin giwar tekun.
An gano gawar giwar tekun mai tsawon mita 9.5 a cikin tekun da ke kusa da tsibirin Kapota a gundun dajin Wakatobi a ranar Litinin.
Ana binciken halittun da matukiyar jirgi ta gani a sama
Biri ya kashe wani jariri a Indiya
Kifi ya kashe wani mutum bayan ya cece shi
Gano giwar tekun ya haifar da damuwa tsakanin masu fafutukar kare muhalli.
Kamfanin dillancin labarai na AP ya ce Dwi Suprapti, wata jami'a da ke kare hakkokin dabbobin ruwa a WWF a Indonesia, ta ce: "Ko da yake ba mu iya gano dalilin mutuwar giwar tekun ba, amma abubuwan da muka gani da idanuwanmu ba su da kyawun gani."
Ta kuma kara da cewa ba zai yiwu a ce robobin da giwar ta hadiye ne dalilin da ya haifar da mutuwar giwar ba saboda yanayin rubewar da ta yi.
A cikin wani sakon da asusun tallafin gandun daji WWF ya wallafa a shafinsa na Twitter ya yi bayani dalla-dalla kan abubuwan da aka gano a cikin dabbar:
"Roba mai karfi (guda 19 mai nauyin giram 140) da kwalaben roba (guda 4 masu nauyin giram 150) da jakankunan roba (guda 25 masu nauyin giram 260) da takalman roba (guda 2 masu nauyin giram 270) da zararruka masu nauyin kilogiram 3.26 da kuma kofunan roba (guda 115 masu nauyin giram 750). "

Labarin Mamma Barka

 Laraba da safe ne Allah Ya yi wa sanannen mawakin nan na Jamhuriyar Nijar, Mammam Barka rasuwa a Yamai babban birnin kasar.
An haife shi a shekarar 1959, ya kuma yi fice wajen yin wakokin gargajiya inda har aka san shi a duniya.
Tuni dai dimbin mutane a jamhuriyar Nijar suka fara bayyana jimaminsu bayan mutuwarsa.
Mai shekara 60 da haihuwa, shahararren mawakin ya bar mata daya da 'ya'ya 10 - mata biyar, sai kuma maza biyar.
Ya fara sana'ar wakarsa ta hanyar amfani da gurumi.
Amma a shekarar 2002, sai ya sauya hanya saboda samun daukar nauyin karatu da ya samu daga Hukumar UNESCO
Ya yi amfani da kudin don sake farfado da kida ta amfani da abin kida na biram, wanda mutanen Boudouma suke amfani da shi - wato masunta a wajen yankin Tafkin Lake.
Ya hadu da wanda ya fi kowa iya amfani da biram, Boukar Tar, wanda ya koya masa yadda ake amfani da nau'in, wanda aka yarda yana kare ruhun tafkin.
Barka ya sa irin wannan kida ya yi tashe "inda ya ja hankalin duniya a kan yadda yake amfani da kayan kidan da ya harhada", a cewar Soas a shekarar 2009.
Ana sa ran za a binne marigayin a garin Tesker a ranar Alhamis.
An san shi da rera wakokinsa a harshen Hausa da Faransanci.
Wannan ita ce daya daga cikin wakokinsa na farko, Ameram - inda yake yabon kirkin wata mata da ya taba haduwa da ita lokacin da yake malami- aikinsa na farko.
Barka ya kuma kasance marubucin littattafai uku a kan al'adun Nijar.
A karshen rayuwarsa ya koya wa mutane yadda ake amfani da garaya.

Labarai duniya :: An sanya dokar hana fita a wasu yankuna a Bauchi

Gwamnatin jihar Bauchi da ke arewa maso gabashin Najeriya ta ce ta sanya dokar hana fita da daddare sakamakon rikicin da ya barke a birnin Bauchi.
Mai magana yawun gwamna Abubakar Mohammed, Malam Ali M. Ali, ya shaida wa BBC cewa "an hana fita tsakanin karfe bakwai na dare zuwa shida na safiya" sanadiyar fadan da ya kai ga mutuwar mutum uku.
Lamarin ya faru ne lokacin da aka samu rashin jituwa tsakanin matasan da suke bikin tunawa da ranar haihuwa kan wata budurwa, amma fadan ya rikide zuwa na kabilanci da siyasa.
Ba za a yi zabe ba sai an dakatar da gwamnan Bauchi - 'Yan takara
Giwaye sun kashe mutane a Bauchi
Abubuwa biyar da ba su da dadi a mulki - Gwamnan Bauchi
Dokar hana fitar ta shafi unguwannin Kagadama da Lushi da Tsakani da Kusu da kuma Anguwan Ngas da ke yankin Yalwa a cikin birnin na Bauchi.
Wanne ne karon farko da aka samu irin wannan yamutsi da ya yi dalilin mutuwar mutane tun da gwamnan jihar ya hau kan mulki shekara uku da rabi da suka wuce, in ji mai magana da yawunsa.
Ya yi kira da mazauna jihar su ci gaba da zama lafiya da juna.
Tuni dai gwaman jihar ya kai ziyara yankunan da lamarin ya shafa.
Gwamna M A ya kuma ce gwamnati za ta yi iyakar kokarinta don ganin rikicin bai yadu a wasu wuraren ba.
Jihar Bauchi dai na daga cikin jihohin da ba a faye samun tashe-tahsen hankula kowane iri ba a Najeriya.

Monday, October 29, 2018

HALIFA SK KISANI A RUHINKI TA WAKA FILM BAKON YANAYI

Wednesday, July 25, 2018

Post hello! He ar u at hm?